✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Warkokin wuru-wurun wankiya

Jona-tantin jirgiya Jagwalgwalon jagaliya Jajjagen jerengiya Jimamin jar miya Juwa-juwar jan-jikin jinya   Warkokin wuru-wurun wankiya Wa-ka-ci-ka-tashin waskiya Wautar watangaririya Warwarar wariya Wukar waftar wukiya…

Jona-tantin jirgiya

Jagwalgwalon jagaliya

Jajjagen jerengiya

Jimamin jar miya

Juwa-juwar jan-jikin jinya

 

Warkokin wuru-wurun wankiya

Wa-ka-ci-ka-tashin waskiya

Wautar watangaririya

Warwarar wariya

Wukar waftar wukiya

 

Dama-damar danne dukiya

Daddako dakin daukakkiya

Dirkaniyar tsiya

Dari-darin damarar dawainiya

Dokin damfara mutan Haurobiya

 

Kundin jona-tanti

Kakarin cin kwakwameti

Kasar kwamin-titi

Kariyar kareti

Ki fadin daga sauti

 

Ina bayanin ’yan sane

Ko sai an yi zane-zane

Nasan kana sane

Nauyinka ka kankane

Batun Mace-da-zane

 

Ko Samun-Bom-da-sauki

Tsaro ya samu tarnaki

Barade sun yi halin na-ki

Jama’a an banki buki

An yi ta lakaki

 

Bambamin Bobon kin bokoko

Miyagu na ta’adi a loko

Shagaban Gudun-loko

Talaka ya rasa na-koko

Akai ta nunke gawa a akoko

 

Dundumin dama-damar damo

Uwargida ta gaza nadin gammo

Uwargada kankambarta tai amo

Jiga-jigan danboto sun yi lamo

Babu mai ce wa baragurbi a kamo

 

Wuru-wurun-Bebe

Namijin fara babe

Shawagin kan masu sassabe

A mayar da wuka a kwabe

A daina lalube-lalube

 

Zazzabin zabe-zabe

Karume-karumen karbe-karbe

Shan kunun kurbe-kurbe

Kumbiya-kumbiya a kebe

Tonon silili ne a tube

 

Make-maken makaho

Bai ganin shawagin shaho

Boyayyun matsabbai a sanho

Ba a biyan lanho

Huhun ma’ahu hohoho

 

Uban-Mama

Kai wa tsama

A zabi-sonka babu kima

Batunka babu makama

Akwai dai sha’awar gulma

 

Danboto ne alama

Rumfar ’yan zalama

Masu kwakwar kwalama

Sui ta dama-dama

Har su afka duma

 

Tsintsiya ce dama-dama

Kai da dama

Tunda Baba ya kama

Ai ta rikon ragama

Da dakile karfin rigima

 

Ba masu takama

A dandalin sandar sunguma

Inda ake ta fama

Da samarin ragamar rakuma

Kirinkin akalar fankama

 

Walle-walle a faifai

Wala-walar kamfai

Kwaramniyar kuffai

Lullubin laftun littattafai

Ko kidan garmahon faifai

 

Cikin watan Noman-Baba na shekara ta dubu karamin lauje da sili da madambaci, yayin da Baban-burin-huriyya ke ta fafutikar ganin Haurobiyawa sun himmatu ka’in-da-na’in wajen fardar garka da gayauna, shi kuwa tsohon shagaban GUDUN-LOKO DA JONA-TANTIN mulkin mulaka’un danboto da sanda jirge sai faman SUKA-DA-BURTSATSEN BATUTUWA yake ta BAMBAMI BUTU-BUTUN BABATU a WARKOKIN WURU-WURUN WANKIYA, inda ya kwata WATSATTSAKEN WASIKAR WASKIYA, irin wadda su Baba-Ojo mai gonakin Ottawa da Baban burga da baragada na tsaunin Mina-mina a Jihar Ni-na-ja suka taba kwatawa a banan nan.

Ganin Gwamnatin Baban-burin-huriyya da ke jan ragamar Haurobiyawa, don kawar da mummunar rigima ta ki yarda ta shiga TATTAKIN TAKUN TUDUNKAR TANKIYA, wajen mayar da martani kan sukar lamarin da Gwanin Gudun-loko ya yi wa Farfesa Ja-gaban zabin-sonka, shi ya sa wannan farfajiya ta nusar da al’umma dabarbarun watsattsake da fallen shafukan mujallu da makalu da wagagen littattaffai ba za ta yi wata kakkausar suka ga tsohon Shugaban Haurobiyawa ba. Sai dai wani HANZARIN HAWAINIYA BA FALLE FADEN KOLON DODON KODI BA, muna masu ankarar da tsohon Shugaban Kasar nan kan lallai ya himmatu wajen faskaren ma’anonin fannonin da ya fi kwarewa, musamman lamuran da suka shafi kamun TAWADA DA RAJIYA da sauran nau’ukan manyan kifayen da suka saba da WUTSIL-WUTSIL da WUTSILA GUDI-GUDI A MALIYA.

Haurobiyawa wanda duk ya ki jin BARI, to ba ya taba yin hannun riga da HOHO ba.

Wai shin ’yan makarantar Dodorido idan har wadanda suka fasko kiren karairayin da Shagaban Gudun-loko da Jona-tantin mulki ya baza a sabon kundinsa, musamman in an yi la’akari da TSANTSAMEWAR TSAMAR DA YA YI WA UBAN-MAMA: JIKAN KENYAWA, JAGORAN AMURKAWA, ai sai a yi masa martani da WURURUN-BEBE, har ma wadansu su ce ya kasura ya zama BABE NAMIJIN FARA.

Batun ingarman karafunan titin tarragon kwangirin layin dogo, ba tare da lakakin jan kafar hannayen agogo ba, ina batun ’yan sane, wadanda suka yi kane-kane wajen wawushe lalitar kasa, tun kafin al’umma su yi aune. Mun dai fasko baragurbin al’umma irin su MACE-DA-ZANE da SAMUN-BOM-DA-SAUKI , wadanda suka kara ta’azzara bambamin bama-baman haramta BOBO DA KWAMBON BOKOKO, inda suka haifar da tarnaki a GABASHIN AREWATAWAN HAUROBIYA, musamman Jihar Bararon-nono da ke Babban birnin Alan-guburo. Kai a zamanin mulkin mulka’u na Jama’iyya mai dan boto da sanda jirge, ’YAN MATAN JABA DA SAMARIN KUSU sun samu walwalar tsuwurwurta wala-walar wulwulawar walankeluwa lakume dukiyar Haurobiyawa.

’Yan makaranta mu kyale tsohon Shagaban Kasar nan ya wancakalar da sabon kundinsa, domin masu nazari, sun tabbatar da cewa mawallafin ya yi rawar dan mazari ko da kiren kanzon kurege ya kattaba domin an samu tabbatacin cewa bai yi cikakken bin kadin lamuran da ya bijiro da su ba. Wadansu ma cewa suka yi bai ma karanta watsattsakensa ba.

Ko ma dai mene hakikani lamari mu yasar da sabon Kundin Gudun-loko da Jona-tantin mulki. Ka da mu sake mu baza wadannnan warkoki ko da a MAKARANSUWA, don gudun yada JUHALA! Muna fatan zai ci gaba a dundume kururu da GAJALA, har ya samu ya sakata ya WALA ya yi ninkaya acikin KWALLA, yai ta zubar da KWALLA bayan an ci masa KWALA!