✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yadda ake fargabar karancin man fetur a Abuja

Mazauna Abuja na zullumi amma NNPC ta ce tana da isasshen man fetur da zai kai wata biyu

Masu ababen hawa a Abuja su na gogoriyon sayen man fetur da zai dauke su tsawon lokaci bayan wayi garin Talata da yawancin gidajen mai a rufe.

Aminiya ta ga dogayen layukan ababen hawa a wasu daga cikin gidajen man da aka bude Abuja, inda mazauna ke zullumin yiwuwar karancin mai sakamakon tashin hankalin da zanga-zangar #EndSARS ta haifar.

Wasu daga cikin masu ababen hawan sun ce tun da sanyin safiya suka je domin su sha mai saboda tun da dare suka lura da alamun karancin mai a gidajen.

Ana iya tunawa a makon jiya Kungiyar Dillalan Man Fetur ta IPMAN ta yi gargadin yiwuwar samun karancin man fetur a Najeriya.

IPMAN ta ce hakan zai iya faruwa ne sakamon harin da masu zanga-zangar #EndSARS suka kai wa motocin dakon mai da wuraren ajiyarsa.

Sai dai sanarwa da Kamfanin Mai na Kasa (NNPC) ya fitar a safiyar Tatala ta ce babu kamfanin na da isasshen mai a rumbunsa kuma bukatar fargabar da masu ababen hawa ke yi.

“NNPC na tabbatar muku cewa yana da sama da Lita biliyan biyu na man fetur a ajiye domin tabbatar da ba a samu karancinsa ba daga yanzu har zuwa kwana 60 masu zuwa, saboda haka bukatar sayen mai saboda fargaba da ake yi”, inji sanarwar.