Wasu ‘yan bindiga da ake zargi ‘yan Boko Haram ne sun kai hari garin Katarko mai nisan kilomita 20 zuwa Damaturu babban birnin jihar Yobe, inda suka bankawa gidaje wuta.
Zuwa yanzu ba a tabbatar da rasuwar wani mutum ba lokacin harin.
Maharan dai sun shiga garin ne ranar Talata da yamma a motoci uku kirar Hilux, inda suka fara bude wa jama’ar garin wuta da bankawa gidajensu wuta.