Wasu ‘yan bindiga da ba a tantance ko suwaye ba sun kai hari fadar Mai Unguwar garin Kaduni Muhammad Bayero, da ke gundumar Langai a Karamar Hukumar Mangu ta jihar Filato a daren jiya Lahadi.
Mai Unguwar wanda rawanin Rit Kadunu, ‘yan bindigar sun harbe shi ne da misalin karfe 8:10 na dare yayin wani da yake zaune a fadar aka yi kuskuren harbinsa a kafa.
A yayin da tsohon Kwamishinan harkokin kasuwanci da masana’antu na jihar Honorabul Yakubu Idi Usman, yake bayyana takaicinsa ga manema labarai ya ce an yi jana’izar Mai Unguwar a safiyar yau Litinin kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.