Wasu ‘yan bindiga sun kashe mutum biyu a kauyen Ambe Madaki a lardin Gwantu na karamar hukumar Sanga ta jihar Kaduna.
Wadanda suka kashe su ne Ibrahim Manzo mai shekara 70 da dan uwansa Barnabas Musa mai shekara 45.
Shugaban karamar hukumar Sanga Mista Charles Danladi, ya tabbatar da aukuwar lamarin inda ya yi Allah wadai da harin ‘yan bindigar.