A daren ranar Talata wasu ‘yan bindiga sun kashe mutum 20 a kauyuka uku da ke karamar hukumar Kankara ta jihar Katsina.
Kauyukan da aka kai harin sun hada da: Dan Marke Z, da Dan Sabau da Karya wadanfda suka hada iyaka da jihar Zamfara.
Shugaban riko na karamar hukumar Anas Isa ya tabbatar da kisan gillar da aka yi wa jama’an kauyukan, ya kuma ce, ‘yan bindiga sun budewa jama’ar kauyen wuta ne daga bisani suka kashe masu dabbobin su.