Gwamnan jihar Zamfara Abdulaziz Yari ya bayyana cewa, ‘yan bindigan da suke fashi da makami a jihar suna da makamai fiye da sauran jami’an tsaron jihar.
Rahotanni na bayyana cewa, a shekaru biyar da suka shude jihayr Zamfara na fuskantar barazanar ‘yan bindiga inda aka kashe dubban jama’ar jihar, yayin da garkuwa da jama`a ya zama ruwan dare a jihar.
A yayin da Gwamna Yari ya gana da shugaba Buhari a fadar shugaban kasa Abuja, ya bayyanawa manema labarai cewa, a cikin daya daga moboyar makaman `yan bindigar sun gano sama da bindigogi 500 kirar AK-47.