’Yan majalisar dokokin jihar Nasarawa (NSHA) a yau Litinin sun sake zaban Alhaji Ibrahim Balabare Abdullahi a matsayin Kakakin majalisar. Sabon Kakakin Majalisar na wakiltar mazabar Umaisha da Ugya da ke jihar.
An zabi sabon Kakakin majalisar ne ta hanyar amincewar duk ‘yan majalisun, yayin da Akawun Majalisar Mista Ego Maikeffi Abashe, ya rantsar da Kakakin tare da Mataimakinsa Mista Tsetse Dandaura daga karamar hukumar Akwanga ta Arewa.
A jawabin Kakakin majalisar ya godewa sauran ‘yan majalisar da suka amince da zaban shi a matsayin Kakakin majalisar a wa’adi na biyu.