Rundunar ‘yan sanda ta Jihar Kaduna ta sanar da cewa ta kama wadanda ake zargi da yin garkuwa da Sheikh Algarkawy tare da kashe ‘yan sanda guda 4 da suke aiki a bangaren binciken masu garkuwa da mutane.
Kamar yadda Daily Nigerian ta ruwaito, ‘yan sanda sun kama a tare da wadanda ake zargi, bindigu guda biyu kirar AK 47 a wajen Shafiu Abdullahi wanda shi ne shugabansu, da kuma Umar Suleiman wada ake kira Wada.