✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Yan sanda sun kama wadanda suka yi garkuwa da Sheikh Algarkawi

Rundunar ‘yan sanda ta Jihar Kaduna ta sanar da cewa ta kama wadanda ake zargi da yin garkuwa da Sheikh Algarkawy tare da kashe ‘yan…

Rundunar ‘yan sanda ta Jihar Kaduna ta sanar da cewa ta kama wadanda ake zargi da yin garkuwa da Sheikh Algarkawy tare da kashe ‘yan sanda guda 4 da suke aiki a bangaren binciken masu garkuwa da mutane.

Kamar yadda Daily Nigerian ta ruwaito, ‘yan sanda sun kama a tare da wadanda ake zargi, bindigu guda biyu kirar AK 47 a wajen Shafiu Abdullahi wanda shi ne shugabansu, da kuma Umar Suleiman wada ake kira Wada.