Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta musanta rahoton da ake ta yadawa a kafafen sadarwar yanar gizo, wanda ke cewa masu garkuwa da mutane sun sake yin garkuwa da wasu mutum 13 a hanyar Kaduna zuwa Abuja. Rundunar ta ce, ana yada wannan rahoton ne kawai don a tsorata matafiya hanyar.
Sai daki rundunar ta sanar da cewa, wasu ‘yan bindigar sanya da kayan sarki na soji inda suka shiga cikin wani gida a kauyen Dutse da ke Karamar Hukumar Chikun a jihar Kaduna ranar 23 ga Satumba 2019 da misalin karfe 1:30 suka sace mutum shida wanda har yanzu ba a san inda suke ba, kamar yadda jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Kaduna ya sanar.