Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta tabbatar da kame dan sandan da ake zargi da harbe wani matashi mai suna Zaharadeen Sammani wanda ke karatun likita a kasar Indiya.
Mai magana da yawun Rundunar ‘yan sandan a Kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya shaida wa Aminiya cewa dan sandan da ake zargi yana tsare a hannun Rundunar ‘yan sanda.” Bayan kama dan sandan zamu tabbatar da an yi adalci.” In ji shi.
Matashin Zaharadeen, ya gamu da ajalinsa ne bayan da takaddama ta barke a tsakaninsa da Dan sandan wanda ya harbe shi a kirji a daura da hotel din Royal Tropicana da ke kan titin Niger a Kano a ranar Larabar da ta gaba ta, a lokacin a aka garzaya da shi asibiti a nan Allah Ya karbi ransa.