✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Yar Najeriya da aka sayar a matsayin baiwa ta dawo gida

Wata ‘yar Najeriya da aka sayar a matsayin baiwa a kasar Lebanon, Temitope Ariwolo ta dawo gida a ranar Asabar. An dawo da Temitope ne…

Wata ‘yar Najeriya da aka sayar a matsayin baiwa a kasar Lebanon, Temitope Ariwolo ta dawo gida a ranar Asabar.

An dawo da Temitope ne tare da wasu ‘yan mata ‘yan Najeriya ta filin jiragen sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.

Temitope da sauran matan sun samu tarba daga shugabar hukumar yaki da safarar mutane da kungiyoyin fararen hula da jami’an gwamnatin jihar Oyo da ‘yan majalisar wakilai.

An dawo da su ne sakamakon sa baki da gwamnatocin Najeriya da Lebanon suka yi tare da sauran masu ruwa da tsaki.