✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yayyafin yarfen yaukaka yamadidi (2)

Mai uwa da makarbiyar Nomau na-manomi a fadin Haurobiya ya yi subul da bakan kassara kudin kwanon kalacin kumallon ranin damina, don haka a birnin…

Mai uwa da makarbiyar Nomau na-manomi a fadin Haurobiya ya yi subul da bakan kassara kudin kwanon kalacin kumallon ranin damina, don haka a birnin Dabo inda ba a dabo aka yi ta yi masa yayyafin yarfen yaukaka yamadidi, sannan aka ci gaba da ce-ce-ku-cen SARE-SAREN SASARIN

SANGARCEWAR SAGARAFTUN SUNKURUN SAUTUN SAFARAR SUFURIN SAMFARERA da SHASSHEKAR SHANTAKEWAR SHA’AWAR SHASHANCIN SHISSHIGIN SHAKIYANCIN SHIKAR SHEKE SHANSHERA, don gudun SHA’ANIN SHUKE-SHUKEN SHEKARA.

Al’amura ne da suka kara ta’azzara yayin da Sabon mutumin Shanono ya yi furucin farin cikin yadda al’umma ke iya dundume kururu da ’yan matsabbai kalilan da ba su haura Hauro kofar hanci da zagaye ba. Duk da cewa ya gindaya iya a birnin Dabo, sai aka yi ta kwakwazo, musamman ma ganin cewa a wannan tsohon birni ba a dabo, domin dolen-dole a kashe taro da kwabo; ga shi tuni aka kakkabe kwabbai, aka yi motsin mutsuttsuke matsabbai, har ma da tsibi-tsibin tsatsubar tsunburburar tsubbace-tsubbace tsagwagwa.

Batun Nomau Na-manomi mai mukamin jan ragamar fardar garkar gayauna, tare da kai-kawon kiwon tsilli-tsillin tsuntsaye da bunkasa busassun bisashe a fadin Haurobiya, ana ta yi masa TEREREN TUMAR TUNZARA TAKURAR TUNKUDO TABAHUWA, musamman ma jin cewa bai musa wannan batu da aka baza bazo-bazo a shafukan shimfida shaci-fadi ba. Kuma su ma kafofin kwakwazon kaudi da mujallun makalutun makatar makalo makalu ba a bar su a baya ba.

A matsayina na Direban allin farfajiyar faskaren fikirar furuci a mikakkiyar makekiyar makarantar dogewar dundumin Dodorido da ke ninkayar nakaltar nunin nusar da watsattsake da falle wagagen littattafai, ya zame mini tilas in baje batutuwa a faifai. Domin ta haka ne kawai mahankalta za su magantu da maganganun masu mukamin mika makamin mutsuttsukar mamungar torokon tokare tartsatsin taratsin tulluwar toliyar tabahuwa, tare da fatattakar firgicin fitintunun faman fankamar Fukuyuma daure da Janjamin jajirtatun jariman Japanawa.

Jerangiyar jimamin jin jimurdar ja-in-jar jama’a ba sabon lamari ba ne a Haurobiya, musamman in an yi la’akari da batun JIBGIN JIBAR JITA-JITAR JIRGA JIGARI-JIGARIN JAMA’A, wanda aka tsiwurwurta a makonnin da suka yi walwalin-waliyon walankeluwar wa-ka-ci-ka-tashin wautar wurge-wurgen watangaririyar wasa wukaken wuccikewa.

A da muna ’yan dugwi-dugwi, ’ya’yan Inna da Baba, mun sha jin ana tallar kayan dumdume kururu da karfin karaji karara, wato:

 

Tsautsayin tsimin tsiwar tsiya-tsiya

Ya damu da gaya

Koko!

Koko!

ko

Kunun tsamiya!

Don tumbatsar tumbudin tumbin tambaya, saboda turnukun tafarfasasshen hatsin hadidiya. Kuma a wancan zamanin sai mutane su tataru a ’yar yara ko farfajiyar kofar gidan mai tuwo da dangauda da tubani da dan wake, inda kowa kan mika sulallansa a jinka masa kayan artabun fatattakar tabahuwa. Sannan ya yi makwalwar kwat-kwat ya kwankwadi na-kwadi, sai kawai mutum ya yi zumbur, ya yi SHAMUWA MASHA RUWA WUYA MIKE!

A halin yanzu dai lamarin ya sha bamban, don ba sauki, in dai ba kwananan da aka yi muku albishiri sayen kwalam da makwalshe da nau’ukan kayan dundume kururu a kan rangwamen rahusar Hauro kofar hanci da zagaye, amma an zo daga bisani ana ta zagaye-zagaye.

Abin bin bahasi a nan, shi ne, shin tabahuwa ce ta ta’azzara ko kuwa talalar talauci ce ta dabaibaye al’umma? Haurobiyawa mai dakin daukakkiya ba ya da cikakkiyar masaniya, tamkar mai dakin na asali, wanda ya san inda ruwa ke yi masa yoyo. Tunda mun gaza tantance tsaba da tsakuwa, tabbas kafafen yada kwakwazo da watsattsaken laftun labarai a kasar Haurobiya, su za su warware mana baki da fari ko in ce ‘zare da abawa.’

Amintacciyar jaridar kasar Haurobiya, tare da uwar gijiyarta Dalilin-taronsu, sun yi tsokaci kan tumbatsar tabahuwa a fadin kasar nan. Duk da cewa wadannan jaridu na da mahangar madogararsu, ni na fasko cewa rashin motsin matsabbai ne ya haifar wa al’umma tumar tambotsai domin akwai dimbin kayan dundume kururu an karkasa kashi-kashi a kasuwanni, illa dai kawai Haurobiyawa masu karamin karfi ba sa iya saye. Kodayake na san wasu na iya cewa, ai ba cinya ba, kafar baya ke nan. Ni dai na fasko cewa, ana dai faman fatara a karkarar kakarar kara, inda a birane ake ta kokarin rage tabara, amma duk da haka mahunkuntan Haurobiya sun yi nisan kin jin karajin kiraye-kirayen kira, har ta sa tagomashin tarin tallafin ya faskara a tsakanin al’umma.

’Yan makaranta, ta yiwu da zarar an tabbatar da karin kadagon kwadagon koto a shawo kan wannan matsalar, musamman idan Malam Na-Agege ya yunkura wajen ganin an jinka wa masu laluben karin kadagon kwadago tallafin kayan dundume kururu su kuwa gama-garin al’umma a yi musu BELIN-AUTA, kan al’amuran da suka danganci tarairayar ’yan dugwi-dugwi a wajen koyon watsattsake da wangalen shafukan wagagen littattafai, a inganta farfajiyar Bokan Turai, don tururuwar tarayyar tarairayar rai.

Da zarar an yi wa al’umma namijin yunkuri, sai a bude dakunan dundume kururu kyauta-kyauta, ba tare da taradaddin rashin matsabbai ba, ballantana a yi ta YAUDARAR YAYYAFIN YARFEN YAYIME-YAYIMEN YADON

YADIYAR YAUKAKA YAMADIDI a kasa, tunda irin wannan takaddamar ba za ta agaza mana da cinikin ciyayyar cin cukubus ko aiken amso alkubus, ballanta a ji dadin hambudar garin bududus ba!

Kuma batun cimuimiyar caka cabin-cabin cokalin cakulkulin cin dadi a kan kudi Hauro kofar Hanci ai ba ta taso ba, domin a manyan gidajen attajirai da ke birnin Dabo, inda ba a dabo akwai wadanda ke tallafa wa raunana a cikin al’umma su dundume kururu kyauta, musamman in mutum ya ziyarci Unguwar Koki-Koki, ko in ce unguwa mai lakabin matar gizo; akwai Hajjaju uwar Marayu da ta shafe shekaru tana fafutikar hana na-mujiyar marasa galihu ya yi zuru-zuru a sanadiyar artabun karon-battar taho-mu-gama da tabahuwa.

Abin tuhuma a wannan gabar, shi ne, bijiro da tambaya kan ko Malam Nomau-na-manomi so yake ya tabbatar da batunsa cewa lallai a kan ingarman karfen karafan karafunan karfa-karfar kafafa yake.

An dai samu rahoto cewa an bude katafaren gidan koto, inda masu ciyayya ke ta hada-hada loto-loto, wato dimbin jama’a sun karkato, har ma ’yan dugwi-dugwi da katoto.

Lallai ina jan na-zomonku, ahir dinku masu neman na-bagas da masu cuku-cukun cin batin-balatin buzuzun bulus, domin akwai yiwuwar a lallaga muku jikkuna lilis, saboda haka a dai kiyayi aikin ibilis a fito da matsabbai ban da kus-kus.

Wannan dai ita ce kyakkyawar dabara, wato batar da kudi, sai kowa ya samu na cin algaragis gudun kada a ruguzo rigis; a dai tada kwanjin karfin taku tinkis-tinkis, har a fafata da tabahuwa ai ragas, wajen cin modar gasa ko ai canjaras!