Hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC ta sanar da cewa, ba a kammala tattara sakamakon zabukan wasu mazabun kananan hukumomin jihar na`yan takarar Gwamna da na ‘yan majalisun dokokin da aka yi ranar Asabar.
Sauran sakamakon zaben da aka yi na kananan hukumomi 17 a jihar wanda aka sanar a yau Litinin na nuna cewa, Gwamna Simon Lalong na jam’iyyar APC ke kan gaba akan sauran ‘yan takarar da kuri’u 44, 929.