✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a yi daurin rai da rai ga masu fyade a Osun

Majalisar Dokokin jihar Osun ta amince da hukuncin daurin rai da rai ga masu aikata laifin fyade a jihar. Haka kuma ta amince a daurin…

Majalisar Dokokin jihar Osun ta amince da hukuncin daurin rai da rai ga masu aikata laifin fyade a jihar.

Haka kuma ta amince a daurin shekaru 14 ga duk wanda aka samu da laifin yunkurin yin fyade.

Shugaban Majalisar Rt. Hon. Timothy Owoeye ya ce dokar wadda a baya aka bai wa jama’ar jihar damar bayyana ra’ayinsu a kai, za ta taimaka wajen magance matsalar yawaitar fyade a jihar.

Za kuma ta ba wa mahukunta kwarin gwiwar hukunta masu laifin tare da hana matasa fadawa cikin mummunar dabi’ar ta fyade, a cewarsa.

“Don haka ina gargadin matasa da su guji dabi’ar nan ta yin kudi a dare daya. Bai dace a rika musguna wa mata ba ko kadan” inji shi.

A karshe Shugaban Majalisar ya yi kira ga matasa su rike ayyukan dogaro da kai domin guje wa shiga miyagun ayyuka.