✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za mu biya Naira dubu 30,500  ga NYSC – INEC

Hukumar INEC ta ce babu bambancin alawus din da za ta biya masu yi wa kasa hidima da za su yi aikin zabe, inda hukumar…

Hukumar INEC ta ce babu bambancin alawus din da za ta biya masu yi wa kasa hidima da za su yi aikin zabe, inda hukumar ta ce za a biya kowannensu Naira dubu 30,500 ne.

Shugaban Hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya sanar da hakan a lokacin da yake bayanin a kan zargin cewa an samu bambanci a alawus din da aka biyan masu yi wa kasa hidimar bayan dage zabe a makon jiya.

A cewar Farfesa Mahmood, duk wanda ya yi aikin zaben yana da Naira dubu 4,500 a matsayin alawus din sanin makamar aiki, sai Naira dubu 1 a matsayin kudin mota da kuma Naira 500 a matsayin kudin abinci na tsawon kwana uku da suka dauka suna sanin makaman aikin.

“Idan kuma aka tura mutum inda zai yi aiki ranar zabe, za a ba su kudin mota da abinci na Naira dubu 9 da 400, wanda ya kama Naira dubu 23 ke nan kowa zai karba. A aikin ranar zaben Shugaban Kasa, za a biya Naira dubu 17,500 ga kowane mai hidimar kasa. Amma tunda ba za a sake koyar da su sanin makaman aiki ba a zaben gwamnoni da majalisun jihohi, sai a biya su Naira dubu 13, wanda idan aka hada jimilla, za a samu Naira dubu 30,500 ke nan,” inji Farfesa Yakubu.