Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-rufai, ya ce mace ce zata iya zama wacce zata gaje shi a matsayin Gwamnan jihar a zaben 2023.
Gwamnan ya ce a yayin da wasu ke tunanin ya fitar da dan takara wanda zai gaje shi, zai iya zabar mace a matsayin wacce zai zaba kamar yadda ya zabi Mataimakiyarsa mace, Hadiza Balarabe a matsayin Mataimakiyar Gwamna.
Gwamna El-rufai, ya kara da cewa, lokaci bai yi ba da zai fara tunanin zaben shekarar 2023. Allah ne kadai Ya san wanda zai gaje shi a matsayin Gwamnan Kaduna.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a yau kafar rediyo lokacin da yake amsa tambayoyin masu saurarensa. Sannan ya ce a yanzu haka akwai mutum 10 da ke da sha’awar neman takarar Gwamnan jihar.