Jam’iyyar PDP ta bukaci Hukumar zabe INEC da ta soke sakamakon zaben Karamar Hukumar Okene da wasu mazabun saboda magudin zabe da suke zargin APC ta tafka a yankunan.
Sakataren watsa labarai na kasa na PDP Kola Ologbondiyan, ne ya bukaci Hukumar zaben INEC da soke zaben musamman Karamar Hukumar Okene
“An zargi APC da magudin kuri’u 112,000 a wasu rumfunan zaben Okene.”