✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zunden Zaman-furfuren Zaman-fara

Zaurancen zunden Zaman-furfure Zagaye-zagayen zare-zare Zubin zungure Zungurun zangarniyar zurare Zaman farar ziryar zaftare   Zabarin zankade-zankade Zankadaziyya ta shide Zillaziyar zille-zille Zillaziyya ta zille…

Zaurancen zunden Zaman-furfure

Zagaye-zagayen zare-zare

Zubin zungure

Zungurun zangarniyar zurare

Zaman farar ziryar zaftare

 

Zabarin zankade-zankade

Zankadaziyya ta shide

Zillaziyar zille-zille

Zillaziyya ta zille

Zogin zungura yai zakwade

 

 Ka da a ce nai kade-kade

Siyasa ce tai mana gande-gande

Wasu za sui lashe-lashe da tande-tande

Mikaku sun baude

 

Garkar gayauna an farde

Ba gara bin zago

Maidan boto ta dago

Harigido hukunci ya tattago

Zaman fargaba aka figo

 

Zaman furfure aka kago

Yarfen yaren Yarin yanka

Mai tsintsiya ta tsinka

Zaren dauri an yaga

Kuri’u sun yi yaga-yaga

 

An yi kiki-kaka

Ciniki ne na furfure

Ba-ni-in-ba ka ba kwanare

Kumbiya-kumbiya ta tattare

Sharar mai kwakwa da ’yar laushi a bare

 

Shigifar shammatar shari’a tai mangare

Hukuncin ga akwai bare-bare

Tufka ce ta warware

Zanzaron zabure-zabure

A daina kobare-kobare

 

A zo ai gyare-gyare

Matsalar kan akaifa

Sakaci ya sa ta fadada

Ganga-ganga tai kugin kida

Har da rade-radin rada

 

An zo ana ta kwafa

A zabi-sonka

An zababbaka

An zabge kuri’un zabuka

An kuma samu baraka

 

An dai yi noman barka

Lamushe gudan bisan kofar hanci

Na adadin kuri’un mutunci

Jaddawalin alkaluman sasanci

Keta haddi ne butulci

 

Damar jama’a ce tabbaci

Kar a yarda da wawanci

Tanadi ko kukutar kunci

An yi wa-ka-ci-ka-tashi

Soke hakkin al’umma da mashi

 

Kun ji almubazzarancin shasanci

Masassara

Marasa galihu na mamular masara

Mutane an sha shakara

Mahukunta masu tattara

 

Mui yunkurin hana fandarar kangara

Baban-burin-huriyya

Hukuncin ga a bibiya

Ko a zauna ba hatsaniya

Al’umma ta san ba danniya

 

Sai mu kara kwazon juriya

Ka da dai a kagara

Sanwa yanzu aka dora

Ka da mugun aiki ya shahara

Lallai mu zabura

Ai zubeben kwarya ba jira

 

Yawan yamadidin yarfen yaren Yari da Zaurancen zunden Zaman-furfuren Zaman-fara ya sanya ala tilas farfajiyar makarantar Dodorido da ke cikin Amintaciyar jaridar kasar Haurobiya ta bibiyi kadin Shari’ar shigifar shammatar sha’anin shugabanci a Jihar Zaman-fara, inda aka karbe ragama daga jam’iyyar tsintsiya aka danka wa mai danboto da sanda jirge. Bisa wannan dalilin ne Direban-alli ya jefa alamar tambaya, kan cewa ko dai Jihar Zaman-fara, wadda a ’yan kwanakin da suka arce ta rikide zuwa Zaman-fargaba, har ta sake rikida zuwa Zaman-furfure?

Gwamna gwarangwam Shehin Shehinnai, mutum ne mai FAGAMNIYAR FANGIMA. Domin sanin kowa ne a fadin Haurobiya kan irin yadda ya yi ta gararambar kai-kawo a cikin gida da kasashen ketare, musamman daidai lokacin da Zaman fara ya gagara, har aka koma zaman fargaba; shi kuwa daga Haurubja sai dai ku ji an ce ya cilla, kamar wata mashillara, ya ketare. Sannan ya zo ya yi kwakyariyar kumbiya-kumbiyar kakaba ’yan takara, har suka rikide, suka zame wa jam’iyyar tsintsiya ’YAN TAKA (KARAN DANI), don haka bayan jama’a sun yi jimirin jefa musu kuri’u, sai Shigifar Shari’a ta ce an kauce wa ka’ida, kuma mulkin mulaka’u na ’YAN KAKABE ba shi da wata fa’ida ga al’umma. Hakika na yarda da wannan batu na kotun koli, amma inda takaddamar take, ai jama’ar da suka yi jimirin dangwale ba a yi musu adalci ba.

Haurobiyawa, tabbas babu tantama an damalmala al’amura a DAMA-DAMAR-DAWURWURIN KURDA-KURDA SIYASAR WASAN SAMSON SIYA-SIYA. Wai da farin faraway ma, mene dalilin gudanar da zabi-sonka a jihar da ake zaman fargaba; masu tada kan adda sun tunkari jama’a gaba-da-gaba? Uwa-uba ga LAMUNIN LUSHEWAR LUMANA, har ta kai ga an yi zaman rashin AMINCIN AMANA.

’Yan makaranta masu koyon watsattsaken falle shafukan kundayen Shigifar shari’ar dokokin lauye-lauye, wajibi ne a kan ku, ku tabbatar da aiwatar da muhiman gyare-gyare, amma ba ’yan gyare-gyare irin na gyare da kurege ba. Sanin kowa ne ana yi irin wadannan dokoki ne don doke tsilli-tsillin tsilla-tsilla tsaka-mai-wuya da al’umma ta samu kanta, bisa tsarin zaman-tattakewa ko sasarin sa-in-sar siyasa da turka-turka tauye tattali. Idan kuwa haka lamarin yake, to da wace manufa aka yi wannan danyen hukuncin kakaba MUTANEN-WALLE-WALLE a matsayin masu jagorancin jan ragamar wakilcin al’umma a Jihar Zaman-fara; ko dai cinikin furfure aka yi tsakanin mai danboto da sanda jirge da mai tsintsiya? Idan kuwa haka lamarin yake, ai sai mu ce cefane ya yi kyau, wato dai ba-ni-in-ba-ka babu kwanare, ko?

Muna fatan dai sabon gwamna gwarangwam Mutanen-walle-walle ba zaI bar al’ummar su yi ta kalle-kalle ba, ta yadda za a sake lalen malalen mulkin al’umma a ba su cikakkiyar kariyar rayuka da dukiyoyi. Hasali ma, lallai ne a samu tabbacin kawar da ZULLUMIN ZALUNCIN ZALAMAR ZABARIN ZULLON ZINARIN ZAMAN-FARA!

Duk da cewa Shigifar shari’ar ta shammaci al’umma wajen yin Zaurancen zunden Zaman-furfuren Zaman-fara, wannan ba zai hana a yi gyare-gyare ba, ta yadda za a kauce wa kwata irin wannan kwakyariyar nan gaba, don gudun ka da a haifar da gaba da giba a tsakanin al’umma, musamman daidai wannan lokaci da Baba zai karkare wa’adin mulkinsa zango na karamin lauje. Sannan duk wanda ya ji cewa, ‘wannan hukunci ya nunke al’umma a baibai,’ to sai a tursasa mahukunta su aiwatar da gyaran dokoki, ta yadda ba za a sake yi mana wala-walar walle-walle ba. Don haka sai mu karkare da jefa kalubale ga jagororin al’ummar Jihar Zaman-fara, musamman Yaron-Mama, mai sarautar Sarar-daukar-dawainiyar Bakin-kura da Malam Na ’Yar mai shinkafi. Fakat!