✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Iran ta harbo jiragen yakin Isra’ila

Iran ta kakkabo jirage marasa matuka a birin Isfahan mai tashar makaman nukilya

Iran ta kakkabo wasu jirage marasa matuka da ake zargin sun kawo mata hari ne daga kasar Isra’ila.

Da talatainin dare ne da aka ji fashewar wasu abubuwan a kusa da filin jirgin birnin Isfahan da ke tsakiyar kasar.

Gidan talabijin na gwamnatin kasar ya ruwaito cewa “an kakkabo jirage uku marasa matuka” a kusa da wani sojoji mai dauke da jiragen yaki samurin F-14 Tomcata a birnin na Isfahan da misalin karfe 12:30 na dare agogon GMT.

Wani kakakin hukumar sararin samaniyan Iran ya shaida wa kafar Aljazeera cewa sun kakkabo jirage marasa matuka, da dama, amma bai yi karin haske ba.

Kafar yada labaran Fars na Iran ta ba da rahoton cewa, gwamnatin kasar ta dakatar da shawagin jirage a kasar sannan ta kunna makamanta na kakkabo jirage da kariyar sararin samaniya.

Amma da daga bisani an dawo da zirga-zirgar jiragen sama yadda aka saba a sasssan kasar .

Ko da yake, kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito Fars na cewa “Ba a san musabbabin karar fashewar abubuwan da aka ji ba, amma ana ci gaba da gudanar da bincike.”

Shirin Isr’aila

Rahotanni na nuni da cewa ita ma Isra’ila, a nata bangaren,  ta kunna makamannta na kariyar sararin samaniya.

Rundunar tsaron Isra’ila ta ce jiniyar gargadin hari sun fara kara a yankunan Arewacin kasar.

Dalilin kai hari Isfahan?

Hari kan cibiyoyin sojin Iran a Syria

Kamfanin dillancin labaran Iran, IRNA, ya ba da rahoto cewa an kai harin bom kan wasu cibiyoyin sojin Iran da ke a Kudancin kasar Syria.

Rahoto na cewa an kai harehare-haren na Syria ne a filayen jiragen soji da ke Adra da al-Thala da kuma wata rundunar soji da ke birnin Adra da kuma kauyen Qarfa.

Hakazalika an ji karar fashewar abuwa a yankin Al-Imam da ke Babel a kasar Iraq.

Zaman dar-dar tsakanin Iran da Isra’ila

Daga bisa ne Isra’ila ta ce za ta dauki fansa kan harin na Iran, wanda ake ganin shi ne ta kaddamar.

Halin da ake ciki a Isfahan

Kafofin labarai sun ba da labarin cewa al’amaru na gudana lafiya a Isfahan bayan harbo jirage marasa matukan da karar fashewan abubuwa da aka da farko.