✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Allah Ya yi wa ‘Bintu’ Dadin Kowa rasuwa

Jarumar ta rasu bayan ta sha fama da rashin lafiya.

Allah Ya yi wa jarumar Kannywood, Fatima Sa’ida wadda aka fi sani da ‘Bintu’ ta shirin Dadin Kowa na tashar Arewa24 rasuwa.

Rahotanni sun bayyana cewar jarumar ta rasu ne a ranar Lahadi, bayan ta sha fama da rashin lafiya.

Wannan na cikin wani sako da Shugaban Hukumar Fina-Finai da Ɗab’i na Jihar Kano, Abba El-Mustapha ya wallafa a shafinsa na Instagram.

Tuni aka yi jana’izarta kamar yadda addinin Musulunci ya tanadar, a unguwar Gunduwawa da ke Kano.

Tuni abokan sana’arta suka shiga yi mata addu’a da samun rahamar Ubangiji.

Wasu da dama kuma sun kadu bayan samun rasuwar matashiyar jarumar.