Fursunoni 228 sun tsere daga gidan yarin garin Koton Karfe na jihar Kogi. Majiyarmu ta samu rahoton cewa, Fursunonin sun tsere bayan ambaliyar ruwa ta rusa wani bangare na ginin gidan yarin.
An dai fara ruwan saman kamar da bakin kwarya da kamar misalign karfe 2 na tsakar daren yau Litinin.
Mai ba gwamnan jihar Kogi a fannin tsaro, Jerry Omodara (mai ritaya) ya ce a yanzu haka an kama fursunoni 100 cikin wadanda suka tsere