An sako dalibai uku da ’yan bindigar Birnin Gwari suka sace a watan Maris 2020 bayan sun dawo daga rubuta jarabawar shiga Jami’a.
An sace daliban ne tare da wata ’yar karamar kanwarsu a kusa da wani guri da ake kira Unguwar Yako da ke hanyar karamar hukumar Birnin Gwari zuwa Kaduna.
A cewar majiyar mu da ke Birnin Gwari, an sako daliban ne uku kusan kwanaki 10 da suka wuce bayan an biya kudin fansa.
Aminiya ta ruwaito labarin sace yaran a cikin watan jiya da yadda ’yan ta’addan suka kashe direban motar da daliban ke ciki mai suna Ibrahim Dawo.