Hukumar ‘yan sandan jihar Osun a yau Laraba sun tabbatar sako jami’an Hukumar Kare afkuwar hadurra ta Najeriya FRSC biyu da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su ranar Lahadi.
Kakakin hukumar ‘yan sandan shiyya DSP. Folashade Odoro, ne ya tabbatar da hakan bayan sako jami’an FRSC a Osogbo babban birnin jihar, sai dai rahoton bai bayyana yadda aka sako jami’an. Kamar yadda majiyar kamfanin Dillancin labarai na Najeriya NAN ta sanar.