Hukumar Yaki da Cututtuka Masu Yaduwa ta Najeriya (NCDC) ta sanar karin mutum 14 da suka kamu da cutar Coronavirus a Najeriya.
Hukumar ta NCDC ta sanar da hakan ne da daren Alhamis a shafinta na Twitter.
Wannan ne ya sa adadin mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar a kasar ya kai 65.