Wasu matasa dauke da muggan makamai sun yi arangama tsakaninsu da matasa masu zanga-zangar #EndSARS a Abuja.
Mutanen dai dauke da gorori da adduna da wukake sun far wa mutanen ranar Asabar suna tsaka da zanga-zangar.
- Babu wanda zai hana zanga-zangar #EndSARS – Shehu Sani
- #EndSARS: Osinbajo ya bukaci masu zanga-zanga su mayar da wuka cikin kube
Tun da farko dai matasan dake zanga-zangar sun yi tattaki a kan titin Gado Nasko dake cikin garin tun da misalin jarfe 7:30 har zuwa karfe 10 na safe.
Lamarin ya janyo cunkoson ababen hawa da ya hada da kananan motoci da kuma na dakon kaya.
Daga nan ne kuma wasu matasa da a ka bayyana a matsayin masu neman a dawo da SARS suka isa wajen dauke da makamai.
Lamarin dai na faruwa ne a lokacin da matasa masu zanga-zangar ke tikar rawa daga wakokin da su ka kunna a motocin da su ka yi amfani da su wajen killace hanyar, a yayin da a gefe guda kuma masu ababen hawa dake cigaba da taruwa ke cike da bakin ciki da fargaba.
Matasan da su ka kai farmakin sun nufi kan masu zanga-zangar yayinda da su kuma masu zanga-zangar suka cika wandonsu da iska sannan aka samu bude hanyar.
Gabanin hakan dai sai da ‘yan sanda suka yi yunkurin shawo kan masu zanga-zangar kan bude hanyar, amma lamarin ya ci tura.