Mayakan Boko Haram, sun kashe sama da fararen hula dubu 27 tun daga 2009 a zuwa shekarar 2019 a yankunan Arewa maso Gabas, shugaban sashen jinkai na Majalisar Dinkin duniya Mista Edward Kallon, ne ya sanar da hakan a wajen taron tunawa da cika shekara 10 da fara rikicin Boko Haram.
Wannan rikicin yafi shafan jihohin Borno, Adamawa da Yobe lokacin kaddamar ginin Majalisar Dinkin duniya a Abuja jiya Laraba.
A yayin jawabin Mista Edward, ya ce harin da aka kai Nganzai a karshen mako wanda ya yi sandiyyar kisan fararen hula biyar na daya daga cikin mummunan harin da aka kai a wannan shekarar.