A yau Laraba shugaba Muhammadu Buhari ya umarci Ministocinsa da su ci gaba da aiki har zuwa ranar Talata 28 ga watan Mayu 2019. Shugaban ya bayyana hakan ne lokacin taron majalisar zartarwa ta kasa FEC da aka yi yau.
Shugaba Buhari ya umarci ministocin da su mika takardun ajiye aikinsu ga Sakataren Gwamnatin tarayya Mista Boss Mustapha, ya kuma ce wannan shine taron majalisar na karshe da suka yi da Ministocin.
Shugaban ya gode wa Ministocin wajen gudunmawar da suka bayar a wannan gwamnatin.
A ranar Laraba ta makon gobe 29 ga watan Mayu za a rantsar da Shugaba Buhari a karo na biyu.