✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Eaglets ta haye gasar cin Kofin Duniya

Kungiyar Kwallon Kafa ta ’yan kasa da shekara 17 wato Golden Eaglets a shekaranjiya Laraba ta samu hayewa zuwa gasar cin Kofin Duniya na ’Yan…

Kungiyar Kwallon Kafa ta ’yan kasa da shekara 17 wato Golden Eaglets a shekaranjiya Laraba ta samu hayewa zuwa gasar cin Kofin Duniya na ’Yan kasa da shekara 17 da zai gudana a Brazil a bana.

Kungiyar ta samu wannan nasarar ce bayan ta doke Angola a wasanta na biyu da ci 1-0.  Kuma kawo yanzu Eaglets ce ta farko a Nahiyar Afirka da ta samu nasarar hayewa zuwa gasar da za ta gudana a Brazil.

Yanzu dai Najeriya ta samu nasara a wasanni biyun da ta yi.  A wasanta na farko da kasar Tanzaniya mai masaukin baki, an tashi ne da ci 5-4 inda Najeriya ta samu nasara, sai wasa na biyu inda Najeriya ta doke Angola da ci 1-0 sai kuma wasan da Najeriya za ta yi na uku a gobe Asabar a tsakaninta da kasar Uganda.

Sai dai wasan na gobe zai kasance tamkar na cika ka’ida ne don komai ya faru Najeriya ta riga ta haye gasar cin Kofin Duniyar a Brazil.

Kasashe hudun da suka kai matakin semi-fainal ne za su wakilci Afirka a gasar ta ’yan kasa da shekara 17 a Brazil a bana.