Gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana shirinsa na baiwa nakasassun jihar ilimi kyauta.
Gwamnan ya bayyana hakan yau lokacin da yake jawabin bikin rantsar da shi, a matsayin Gwamnan jihar karo na biyu. Ya kuma yi alkawarin baiwa ‘yan makarantun firamaren jihar ilimi kyauta.
Gwamna Ganduje, ya ce za a yi wa daliban jihar sassauci da ke karatu a manyan makarantun jihar, kuma zai dora daga cikin ayyuka ci gaba da ya soma a karo na farko, a fannin ilimi, noma, kiwon lafiya da dai sauransu.