✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gingimemiyar ganuwar gane gungun gagararru (2)

A birnin Dabo inda ba a dabo, wadansu na ta jefa azargagiyar zargi kan cewa, an mayar da birnin tamkar mafakar miyagun da ke tafka mummunar…

A birnin Dabo inda ba a dabo, wadansu na ta jefa azargagiyar zargi kan cewa, an mayar da birnin tamkar mafakar miyagun da ke tafka mummunar ta’asa a sassan kasa, har ta kai ga ana ta baza irin wadannan zantuttuka zururu a shafukan zumun zumuntar sadarwar likon alakar na’urori masu kai-kawon hadakar kwanya. Sanannen lamari dai shi ne labarin damke makirin mugun Jihar Tarba-tarba, wanda ya yi awon gaba da Magajin Garin Daurama da aka yi kwanan nan a Unguwar Huta-roro da ke kwaryar birnin Dabo, shi ya haifar da surutu rututu a farfajiyar tukin tuwon titi da Fuskar fuskantar bokoko da Watso-zuffa.

Wai abin da kawai ake ta hankoron nusar da al’umma shi ne, akwai Gungun gagararrun gare-garen gangaren gaftarar gutsirar garu da ke ta fankamar fetsarewar fandararru da suke ta fantsamar fitsararru, masu karfa-karfan kadangaru a Zirin zungurar zungurun Zankaleliyar zangarniya zururu, inda ake ta tsiwurwurta zaman-takewa zuru da zullumin zalamar zakwadin zakaru a cikin jerin jihohin jama’ar jamhuriyyar jimamin  jamhuru da ke birane da kauyuka, inda batagari ke ta tufka; ga turmutsitsin jama’a ba masaka, har dai aka samu baraka, ta yadda wani ba zai yi kishin kasarka ba; matukar kai ba ka san naka ba.

Ganin yadda al’amura suke ta kwan-gaba, kwan-baya, sai na ce a daina kwafa  domin wanzami ba ya son jarfa, laifi dai tudu ne, kun ga ke nan shagabanni (ban ce shugabanni ba, a’a masu shan gaban al’umma) sun sha’afa, kuma sun shafa wa gemunsu ruwa, alhali na talakawansu na cin wutar balbalin bala’i, inda aka yi musu kawanya, har suka dauki duwarwatsu suna ta jifa, amma tsilli-tsillin tsiyataku sun yi musu kukutawar kundumbalar kudundunen hangame hancin shakar kirfa.

Don haka ma wadansu ke ta tsirfa kan matsala tun tana kan akaifa, inda aka ki shafa mata ruwa ko kura ta lafa, sai ma aka kara jawo mayafin musifu aka yafa har kowa ya fara takewa da kafa.

Tsiwurwurta tsirin tsiyatakun makirce-makircen maboyar miyagun macuta, ta kai al’umma na ganin tamkar birni mai dadadden tarihi a kundin labaran da, da na yanzu ya zamo wata mafakar munafukan makiran magabta mamugunta. Batu na ingarman karfen karafunan kwangirin dogo, lallai mu yi hanzarin fuskantar fahimtar fasko cewa, irin wannan wurin boye-boyen bata-gari a kwai shi a daukacin fadin Haurobiya, hasali ma a kusan kowace jiha da ke fadin kasar nan akwai wadanda ke da masaniya, illa dai kawai suna fargabar yin tonon sililin wirkilili don kada miyagu su kai musu farmaki.

Arewatawan Haurobiya, kuna jin cewa manyan mutane masu rawunna, irin su Mai martaba Masanin Sisi-da-sisi da Muminin Mai martaba na birnin Dikko; da Shehun Bararon-nono na birnin Madogarin Alan-guburo da Shehun Birnin Lawurje ba su da cikakkiyar masaniyar ana turka-turkar tataburzar takun-sakar tursasa wa jama’arsu da ake yi ba ji, ba gani?

A kimar matsayina na babban direban allin makarantar koyar da watsattsaken wasikun wallafe-wallafen wagagen littattafai, inda ganin na-zomon masu rawunna kar yake ji; na-mujiyarsu na ganin tarau, amma inda gizo ke sakarsa ba tare da taimakon koki ba, shi ne, kimar mukamansu an yi rugu-rugu da ita, har ta kai ga a irin wannan mummunan yanayi ba za su iya yin katabus ba. Hasali ma, masu wasan Samson-siya-siya da kwakwalwar talakawa a tafarkin damo-da-kura-diyya na iya kai musu farmaki, tunda matukar suka tabuka abin a-zo-a-gani, su kuwa guntun bahayarsu ya bushe. Kuma akwai yiwuwar su fuskancin tada kayar baya, har su rasa cinikin cin cukubus da cammar cin cammas.

Shi ya sa ma, tambayar da kan bijiro wa al’umma a lokuta da dama ita ce, idan har managartan mutane suka kasance cikin firgicin faganniyar farmakin miyagun da suka danno garuruwansu, ai da wuya a samu wanda zai kawo musu dauki? Ko jami’an tsaro za su rasa katabus matukar ba a kyankyasa musu kus-kus ba? Uwa-uba ma akwai yiwuwar jami’an su yi kicibis da miyagun, amma rashin sani da aka ce ya fi duhun dare dundumdurundum, sai magabatan da ke cutar da al’umma su arce ba tare da wani cikas ba.

Ko dai ginin ganuwar garkuwar garkame gari za a dawo da shi, tunda iyaye da kakanni sun yi irin wannan tsarin tsaro? Wadansu na iya furta eh, ko a’a, bisa dalilan daddalewar dagar dugunzumar tashin tashinar tunzura jama’a. To alkalami dai ya rigaya ya kame, tunda bayan zuwan Turawan mulkin mulaka’u an rigaya an sare kowane kyaure, ballantana a ce sai an tantance bako da bakuwar da ke hankoron kutsa kai cikin birane da kauyuka. Yanzu abin da ya rage wa al’umma, illa dai, GINE-GINEN GANUWAR GARKUWAR GOGORIYON GARIYON  GANTSARARRUN  GANDE-GANDEN GAFTARE GARU, amma cikin nutson natsuwar nauyaya nunin nusarwa. Shi ya sa ma na hori nagargaru da baje na-mujiya kuru-kuru don yaye duhun jahilcin jahilai da shawo kan dolancin dolaye, masu wautar wulwulawar wawancin wawaye, suna gani ana ta tsiwurwurta maimaicin mummunan makircin mutsuttsuke makomar masanan malamai. Don haka sai mu sake dabara, wajen laluben hanyar gyara, tare da toshe ko da kafar algarara ce, ta yadda za mu yunkura, mu hanzarta kada a makara. Yin hakan na iya tabbatar da GAGARUMIN GININ GINGIMEMIYAR GANUWAR GANE GUNGUN GAGARARRU.

Lallai mu lura ba ma bukatar katafariyar katangar kange kai-kawon al’umma, domin a nahiyar Turai tuni aka bangaje bangon biranen Berlin, inda a yau ya cure ya zama fallen filin farfajiyar gama-garin gamayyar garuruwan jamhuriyyar juyin jan-ragamar jama’ar Jamusawa. Mu ma ke nan a Haurobiya, haramta haramiya da halatta halaliya, bisa tandin dokokin darkake tu’annati za su zamo mana tanadin tunkude ta’adi, musamman in mun dora ta’adar jinjinar jinkan al’umma irin ta zamanin zamunnan magabata, wadanda suka farmaki miyagun mamuguntan macutan magabta.

’Yan makarantar Dodorido da ke falle shafukan mujallu da makalu da watsattsaken wallafe-wallafen wagagen littattafai, da kun baje fahimtarku a faifai za ku fasko cewa, masu martabar mallakin mulkin mulukiyyar gargarjiya na da gagarumar gundumemiyar gudumar gudunmawar da za su ganganda a wannan yanki na Arewatawan Haurobiya, don cin dunun darkakin dumuiniyar garkuwar gagara kuwwa da tashin tashinar tayar da kan adduna a ko’ina cikin fadin kasarsu.

Wajibi ne mu jadadda bukatar ganin jajirtattun jami’an asiri sun himmatu da karin kokari wajen tattara kundayen barbaje bayanan sirri, ba tare da jinkiri ba, tare da jarumtakar jajircewar juriyar jimirin jingine jan-kari. Aiwatar da managartan tsare-tsare za su iya zama sanadi ga birane su yi kasurar kasaita, karkara kuwa ta kambama a yi ta tarairayarta, ta yadda mazaunan unguwanni za su samu kubuta daga zullumin zaman ragaita, inda wasan ’yar burum-burum da magabtan lumana zai kasance kacokan da zakakuran zarata, tamkar yadda can a kasashen duniya aka yi bajintar baje bata-gari da ninkayar nakaltar nunin nuniya, tattare da kwazon hana danniya har mutane suka daina duk wata tankiya, har suka samu rabautar ribatar rabashen romon ragon Romaniya.

Duk mai tababa sai ya binciki birnin Barbados da hayin Honduras, amma dai a bar batun Bahamas, kodayake ma ai ban san me aka yi a Beralus ba, amma dai ina da masaniya cewa, babu bangon Berlin a Jamus, don haka sai mu bibiyi batutuwa bi-da-bin kalmomin kalallame kalaman kasurar kundumbalar kudundune kasurgumin kusumbin kululun kokon kurmusun kalkalewar kare-karen karamin kamus.