An samu tashin gobara da ta kone gidaje a kauyen Barebari da ke karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa, sakataren hukumar bada agajin gaggawa ta jihar (SEMA) Alhaji Sani Yusuf ne ya tabbatar da hakan.
Alhaji Sani ya ce, hukumar SEMA zata magance dalilin aukuwar tashin gobarar wanda ta fara tun daga karfe 11 na safe zuwa karfe 6 na yamma a jiya Talata.
Sakataren ya bayyanawa kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN yau a Dutse babban birnin jihar cewa, gobarar ta kusa kone kauyen baki daya.