Gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita na tsawon sa’a 24 wanda zata fara aiki nan take a garin Kasuwar Magani da ke karamar hukumar Kajuru.
Mataimakin gwamnan jihar, Barnabas Yusuf Bala, ya bada umurnin da a aiwatar da dokar hana fitan yadda kamata. Sa’annan ya bukaci jama’a da su yi da’a wa dokar, kuma su goyi bayan kokarin da a ke na wanzar da zaman lafiya a garin.
An dauki wannan matakin ne bayan wani zama da majalisar tsaron jihar ta yi a yau Juma’a.
An kuma tura jami’an tsaro yankin don tabbatar da zaman lafiya.