Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ta kashe ’yan fashi a yayin da suke kokarin satar shanu a yankin Kuzo da ke Jihar Kaduna.
’Yan fashin wadanda suke wani fili a yankin Gabas maso Yammacin dajin, an kashe su ne bayan jirgin yakin rundunar ‘Operation Thunder Strike’ ya yi musu luguden wuta.
- An ceto ‘yan mata 26 daga hannun masu garkuwa a Zamfara
- An yankewa ‘yan Najeriya 6 hukunci a Dubai kan zargin daukar nauyin Boko Haram
Shugaban Sadarwa na Rundunar Tsaro ta Najeriya, Manjo Janar John Enenchea cikin wata sanarwa ya ce helikoftan soji da ke sintiri a yankin ne ya hallaka ’yan ta’addan.
Sanarwar ta ce, “Mayakan sama na Operation Thunder Strike sun kashe ’yan bindiga da dama a yankin Kuzo da ke Jihar Kaduna, yayin da suke yunkurin safarar dabbobin da suka sata ta yankin” inji shi.