Babbar kotun jihar Kano ta tsayar da ranar 14 ga Nuwamba 2019, a matsayin ranar da za a yanke hukunci game da kalubalantar dokar majalisar dokokin jihar Kano ta kirkiro don bai wa Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, damar kirkikiro karin sabbin masarautu hudu a jihar.
idan ba a manta ba tsohon shugaban marasa rinjaye na majalisar dokokin jihar Alhaji Rabi’u Saleh Gwarzo da Alhaji Babangida Yusuf Sulaiman, sun kalubalanci dokar kirkiro da sabbin masarautun hudu da Gwamnan jihar ya yi.