A jawabin rantsar da Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai a karo na biyu, ya roki jama’ar jihar Kaduna da su yafe masa akan daukan tsauraran matakan da za a yi wajen bunkasa jihar.
Gwamnan ya ce, za a baiwa mata ma’aikatan gwamnati wadanda suka haihu hutun wata shida, don tabbatar da lafiyar jaririn da suka haifa da samun kyakkyawan shayarwa.
El-Rufai ya kara da cewa, wannan gwamnati za ta maida hankali ne akan bukatun ’yan jihar kuma wannan gwamnatin ta kowa ne dan jihar ne.