Hausawa mazauna Jihar Ribas sun rasa mutum biyu a garin Oyigbo, bayan da aka zargi kungiyar masu fafutukar kirkirar Biyafara (IPOB) da kai musu hari.
Rikicin wanda ya faru a ranar Lahadi ya kuma jikata wasu mutum biyu.
Wani ganau, ya bayyana wa Aminiya cewar, a ranar Asabar zuwa Lahadi ne wasu da ake zargin ‘yan kungiyar IPOB ne dauke da miyagun makamai suka kai hari a unguwar Hausawa.
- Sojoji sun fatattaki ‘yan bindiga a Nasarwa da Binuwai
- Sarakunan Arewa na tattunawa kan tsaron yankin
Ya ce sakamakon harin da aka kai, “Mutum biyu sun rasa rayukansu, yayin da aka ji wa wasu biyu munanan raunuka”.
Mai magana da yawun Hausawa mazauna Jihar Ribas, Alhaji Musa Saidu, ya tabbatar was wakilinmu aukuwar lamarin.
Saidu ya ce wasu matasa da ake zargin ‘yan kungiyar IPOB ne dauke da makamai suka kai hari a wani wuri da mafi yawanci mutanen Hausawa ne, a Oyigbo, sakamakon haka aka kashe samarin biyu.
Ya ce sakamakon harin wasu kananan ‘yan tireda biyu sun samu munanan raunuka.