✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ma’aikatan jinya 300 na cikin hadarin kamuwa da Coronavirus a Lagos

Kungiyar ma’aikatan jinya ta Najeriya reshen jihar Legas ta bayyana cewa sama da ma’aikatan jinya 300 ne ke cikin hadarin kamuwa da cutar coronavirus a…

Kungiyar ma’aikatan jinya ta Najeriya reshen jihar Legas ta bayyana cewa sama da ma’aikatan jinya 300 ne ke cikin hadarin kamuwa da cutar coronavirus a Legas.

A cewar kungiyar, zuwa yanzu 16 daga cikin ma’aikatan jinyar sun an tabbatar da sun kamu da cutar yayin da 4 daga cikin su suka warke aka sallame su.

Kungiyar ta shaida haka ne a shafin ta na twitter @LagosNannm, inda ta bayyana cewa ma’aikatan jinya sama da 300 sun sami kan su ne cikin halin hadarin kamuwa da cutar ne a lokacin da suke bakin aiki.

Ta ce, ma’aikatan lafiya da ke kan gaba wajen dakile cutar Coronavirus, kwararru ne da cutar ta cinmmasu a lokacin da suke gudanar da aiyukansu.

A saboda haka tayi kira ga ‘yan Najeriya da su sanya su a addu’a.

Tun a baya dai, kungiyar ta yi kira ga ma’aikatan jinyar a Legas da su kasance masu kiyaye wa a lokacin da suke a bakin aiki.

” Tabbas aikin na yiwa kasa da al’umar ta hidima ne, amma duk da haka bai kamata ku dinga jefa rayuwar ku da ta masoyan ku cikin hadari ba, idan ba a tanadar maku da kayan kariya na aiki ba, kuma ta yi du bi kan hanyoyin da suka dace ku nema a baku, kafin ku duba marasa lafiya.” Inji sanarwar kungiyar.

Sanarwar ta kara da cewa, ma’aikatan jinya nada hurumin kin duba marasa lafiya idan ba a tanadar masu kayan aiki na kare kansu ba.