`Yan majalisar dattawa sun amince da bayar da tallafin Naira biliyan 10 a cikin kudin kasafin 2019 don tallafawa ‘yan gudun hijira da wasu da rikicin `yan bindigar jihar ya raunata.
Maja;lisar ta bukaci gwamnatin tarayya da ta kaddamar da wani kwamitin wucin gadi da zai dinga mikawa shugaban kasa rahoton abin da ke faruwa a jihar Zamfara.
Majalisar ta yi Allah wadai game da abin da `yan bindigar ke aikatawa a jihar.