An tabbatar da rasuwar mutum uku a jirgin ruwa da ya dauki fasinjoji 20 a tsakanin gadar Liverpool da Coconut da ke jihar Legas.
Janar Manaja na hukumar bayar da agaji (LASEMA), Mista Adesina Tiamiyu ya tabbatar da aukuwar lamarin da ya faru ranar Laraba da misalin karfe 8:20 na dare.
Tiamiyu ya ce, fasinjoji biyar sun bace yayin da hukumar ta kubutar da mutum 12.