Yayin da ‘yan Najeriya ke gudanar da zabe a yau Asabar don zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar tarayya, duk da cewar mutane masu yawa sun fito don kada kuri`arsu a yankin karamar Hukumar Dala da ke Jihar Kano, sai dai Na`urar tantance masu zaben ta jawo tsaiko a harkar gudanar da zaben.
A mazabar Yalwa mutane sun fito tun misalin karfe 8:00 na safe inda suka hau layi, sai dai lokacin da jami`an gudanar da zaven suka fito da kayansu sai na’ura ta ki aiki har zuwa kimanin sa’a daya.