Babban limamin masallacin Olohungbebe, Ilorin, jihar Kwara Alhaji Lukuman Abdullahi, ya bukaci musulman kasar nan akan tallawa mabukata lokutan watan azumin Ramadan wanda aka fara yau Litinin.
Limamin ya yi kiran ne a Ilorin lokacin da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai NAN.
A daren jiya Lahadi ne Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar III, ya sanar da yau Litinin a matsayin daya ga watan Ramadan.