A ci gaba da sanar da sakamakon zabe da ake yi yanzu, Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na Jam’iyyar APC ne yake kan gaban dan takarar Jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar.
Ya zuwa yanzu dai an sanar da sakamakon jihohi 16 na Birnin Tarayya Abuja, inda Buhari yake da jimillar kuri’a 6,153,880, shi kuma Atiku yake da kuri’a 5,149,869.
Ke nan Buhari yana gaban Atiku da kuri’a 1,004011.