A yau Laraba majalisar dattawan Najeriya ta dage zamanta akan kasafin kudin shekarar 2019 da aka gabatar mata zuwa makon gobe saboda rashin cikakkun bayanan da ake da bukata.
A ranar Alhamis da ta wuce ne Kwamitin bin diddigin yadda za a sarrafa kudaden da za a kashe a kasafin kudin 2019, wanda Sanata Mohammed Danjuma Goje ke jagoranta suka gabatar da rahoton kwamitin su a gaban zauren majalisar.
A yau bayan da kwamitin suka rahoton su ga zauren majalisar sai suka gano cewa, ba bu cikakkun bayanan abin da kasafin kudin 2019 ya kunsa.