✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Shugabancin Majalisa: Gwamnonin APC sun amince da Lawan, Gbajabiamila

Gwamnan jihar Borno Kashim Shettima, ya ce tsofaffin Gwamnoni da suke majalisar dokokin tarayya sun amince da Sanata Ahmed Lawan a matsayin wanda zai jagoranci…

Gwamnan jihar Borno Kashim Shettima, ya ce tsofaffin Gwamnoni da suke majalisar dokokin tarayya sun amince da Sanata Ahmed Lawan a matsayin wanda zai jagoranci majalisar dattawa.

Gwamna Kashim ya bayyana hakan ne lokacin da yake ganawa da manema labarai a garin N’Djamena da ke kasar Chadi, ya kuma ce zababbun Sanatoci  sun amince da zabar Femi Gbajabiamila a matsayin kakakin majalisar wakilai.

Gwamnan Bornon ya kara da cewa, duk zababbun Sanatoci da zababbun `yan majalisar wakilan tarayya daga jihar Borno suna goyon bayan shugabancin Lawan da Gbajabiamila.