Rundunar sojojin Najeriya ta ce, ta fara maida ‘yan gudun hijirar da ke zaune a sansanin su na Sabon Gari a karamar hukumar Dambuwa a jihar Borno.
Sabon gari ya kai nisan kilomita 34 daga cikin Dambuwa, yayin da kuma ya kai nisan kilomita 100 daga Dambuwa zuwa garin Biu.
Kwamandan rundunar Operation Lafiya Dole , Manjo Janar Benson Akinroluyo ne ya sanarwa manema labarai hakan a yau. Kwamandan ya tabbatar cewa, maida ‘yan gudun hijirar zuwa gidajensu na daya daga cikin ayyukan rudunar a yankin.