Bayan zanga-zangar da `yan kasar Sudan suka yi a sassan a kasar, Sojojin kasar sun tilastawa shugaba Omar al-Bashir sauka daga mukaminsa na shugabancin kasar.
Shugaba Omar, ya shugabanci kasar shekara 30 tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a shekarar 1989.
An zargin Shugaba Omar, da ingiza manyan laifuka ciki har da yaki da sauran rikicin da ya faru a garin Darfur.