✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tukur Wurno ya zama Sarkin Hausawan Oshodi

Ranar Lahadin da ta gabata aka yi kasaitaccen  bikin nadin Alhaji  Tukur  Wurno  a  matsayin Sarkin Hausawan Oshodi, wanda  Sarkin Hausawan Jihar Legas,  Alhaji Aminu …

Ranar Lahadin da ta gabata aka yi kasaitaccen  bikin nadin Alhaji  Tukur  Wurno  a  matsayin Sarkin Hausawan Oshodi, wanda  Sarkin Hausawan Jihar Legas,  Alhaji Aminu  Yaro  Dogara  ya yi  bayan da jama’a suka amince da hakan.
Wani dattijo da ya yi  jawabi  a madadin sauran  jama’a ya bayyana wa sarki Aminu cewa Alhaji Tukur ya dade yana dawainiya a kan duk  wani  abu  da ya shafi Bahaushe da ma duk  wani  dan Arewa mazaunin unguwar ta Oshodi tun kafin a gabatar da sunansa.
Da yake jawabi jim kadan da nadin, Sarki Aminu  ya ce  ya amince da  nada Alhaji Tukur ne saboda shi ne  jama’ar  suka  ce  suna so,  kuma  yana  fata za su yi masa  biyayya, wadda ta ita ce  zai kara  samun  karfin gwiwar ci gaba da yi musu hidima, kamar ko ma fiye da yadda yake yi a da.
Ya bukaci sabon sarkin ya san cewa  rashin  adalci na iya jawo masa da-na-sani, “Domin kuwa  duk shugaban da ba ya adalci,  idan bai ga  hukunci  daga  nan  duniya  ba, to ya sani  cewa  zai koma ga  Allah, don haka ya nemi ya kasance mai adalci  da  hangen nesa wajen tafiyar da mulkinsa.
Shugaban kungiyar Yarabawa zalla (OPC ), Otunba  Gani Adams, wanda ya halarci taron, ya tofa albarkacin bakinsa, inda ya yi  fata za a ci gaba  da samun hadin kai tsakanin sabon sarkin da  jama’arsa. Dangane da dangantakar da ke tsakanin Hausawa  da Yarabawa sai ya yi fata lamarin zai kara kyautatuwa da yake yanzu kowa ya kara ilmin fahimtar rayuwa wajen gane cewa. tashin  hankali  ba abin da yake  samarwa  sai  koma-baya ga al’umma.
Ya yi kira ga al’ummomin biyu da ma  sauran  al’ummun Najeriya,  a  duk  inda  suka samu  kansu,  su  zamo  masu  kaunar  juna, domin ba  wanda  ya fi Allah sanin dalilin  da ya sa Ya yo  mu wuri guda.
Shi ma dan wasan kwaikwayo Chidi Mokeme cewa  ya yi bikin ya kayatar da shi kuma haka  ya kamata  a ce ’yan Najeriya  na zaune, suna kyautata dankon zumunta da ke tsakaninsu.
Emeka Ike, shi ma wani dan wasan kwaikwayo, cewa ya yi yana alfahari  da  yawan kabilun  da  Allah ya albarci  Najeriya da su,  sai dai  fatansa  shi ne  a ci  gaba  da  hankuri  da  zaman tare.
Shi kuma sabon sarki Alhaji Tukur fata ya yi Allah Ya ba shi  ikon daukar nauyin da aka dora masa.  Ya  bukaci  daukacin mutanen  da  suka  halarci bikin su taya shi addu’a don ya kai ga cin nasara.