Hukumar ‘yan sandan jihar Edo ta tsare wani matashi mai shekara 18 akan tuhumarsa na kashe mahaifiyarsa da yi wa gawar fyade.
Wanda ake zargin mai suna Samuel Akpobomen dan jihar Delta yayin da ya aikata laifin a unguwar Ologbo da ke karamar hukumar Ipoba-Okah ta Jihar Edo.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Edo Babatunde Johson Kokumo ya shigar da karar tare da wasu mutum 87 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a jihar.