✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan bindiga sun kashe mutane da dama a Kauyen Zango

Rahotanni na bayyana cewa, a wani sabon hari da ‘yan bindiga suka kai kauyen Zango da ke Karamar Hukumar Kankara a jihar Katsina, an kashe…

Rahotanni na bayyana cewa, a wani sabon hari da ‘yan bindiga suka kai kauyen Zango da ke Karamar Hukumar Kankara a jihar Katsina, an kashe jama’ar kauyen da dama.

‘Yan bindigar sun shiga a kauyen ne tun misalin karfe 6:00 na yamma a jiya Lahadi, inda suka fara kone gidajen jama’a da lalata ganakin su.

Har ya zuwa yanzu ba a sanar da adadin mutane da aka rasa ba, sanadiyyar wannan harin.