Rahotanni na bayyana cewa, a wani sabon hari da ‘yan bindiga suka kai kauyen Zango da ke Karamar Hukumar Kankara a jihar Katsina, an kashe jama’ar kauyen da dama.
‘Yan bindigar sun shiga a kauyen ne tun misalin karfe 6:00 na yamma a jiya Lahadi, inda suka fara kone gidajen jama’a da lalata ganakin su.
Har ya zuwa yanzu ba a sanar da adadin mutane da aka rasa ba, sanadiyyar wannan harin.